in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
HCR: Adadin 'yan gudun hijirar Sudan ta Kudu ya cimma mizalin miliyan guda
2016-09-17 13:16:30 cri
Adadin 'yan gudun hijirar Sudan ta Kudu da suka samu mafaka a kasashe makwabta ya cimma mizalin miliyan guda a wannan mako, in ji Leo Dobbs kakakin hukumar 'yan gudun hijira ta MDD (HCR) a ranar Jumma'a a yayin wani taron manema labarai a birnin Geneva.

Wani karin adadin 'yan gudun hijira dubu 185 sun tsere tun bayan barkewar sabbin tashe tashen hankali a farkon watan Yuli a cikin wannan kasa, in ji kakakin.

Yawancin sabbin mutanen da suka zo sun ratsa kan iyaka domin shiga Uganda, amma kuma an gano wani karin zuwan mutane a yankin Gambella na kasar Habasha a makon da ya gabata, wasu mutanen sun kama hanyar zuwa Kenya, RDC-Congo da Afrika ta Tsakiya. Wadannan kasashe, abin nuna yabo, shi ne sun bar kan iyakokinsu bude domin sabbin 'yan gudun hijirar, in ji mista Dobbs.

A cewar HCR, yawancin wadannan mutanen da suka tsere daga Sudan ta Kudu, mata ne da yara. Daga cikinsu, akwai wadanda suka tsira daga tashe tashen hankali, ayyukan cin zarafin mata da fyade, yara da aka raba da iyayensu ko masu tafiye tafiye su kadai, da nakasassu, da tsofaffi, da kuma mutanen da ke bukatar jinya cikin gaggawa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China