in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 3 sun mutu sakamakon fashewar nakiya a wata kasuwar Somaliya
2016-09-07 09:23:36 cri

Wani jami'in kasar Somaliya ya bayyana a jiya Talata 6 ga wata cewa, an kaddamar da wani harin nakiya a wata kasuwa dake birnin Mogadishu, hedkwatar kasar Somaliya, lamarin da ya haddasa mutuwar mutane a kalla 3.

Ban da wannan kuma, an kai wani harin na igwa, a wani yanki dake dab da fadar shugaban kasar, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula a kalla 4.

Kawo yanzu dai babu wani mutum ko kungiya da ta sanar da daukar alhakin kaddamar da harin, ko da yake kungiyar masu tsattsauran ra'ayi ta al-Shabaab ta sha kai makamantan wadannan hare hare a sassan kasar. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China