in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da taron ministocin harkokin waje a tsakanin Sin da Japan da Koriya ta kudu
2016-08-24 16:17:01 cri
A yau Laraba a birnin Tokyo, babban birnin kasar Japan, ministocin harkokin waje na kasashen Sin da Japan, da kuma Koriya ta kudu sun gudanar da taro a karo na takwas a tsakaninsu.

Wang Yi, ministan harkokin waje na kasar Sin ya ce, kasancewar Sin da Japan, da kuma Koriya ta kudu kasashe masu karfin tattalin arziki a gabashin nahiyar Asiya, suna daukar babban nauyi ta fuskar raya tattalin arziki, da hadin gwiwa da kuma kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a shiyyar.

Wang Yi ya kara da cewa, Sin za ta gudanar da taron kolin kungiyar G20 a birnin Hangzhou, a matsayinsu na muhimman mambobin kungiyar G20, kasar Sin tana fatan kara tuntubar juna da hadin gwiwa da Japan da Koriya ta kudu, ta yadda taron zai ba da taimako ta fannin raya tattalin arzikin duniya da kuma inganta tsarin tattalin arzikin duniya.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China