in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan ta kira wani dandalin yaki da ta'addanci
2016-08-19 10:35:24 cri
A jiya Alhamis ne, a birnin Khortum, hedkwatar kasar Sudan aka kira wani dandalin kasashen Larabawa da nufin dakile ayyukan ta'addanci, inda aka tattauna kan wasu muhimman abubuwa, ciki hadda kara hadin gwiwa ta fuskar tsaro, da yaki da ta'addanci cikin hadin kai da dai sauransu.

Kungiyar hada kan kasashen Larabawa AL da ma'aikatar harkokin wajen kasar Sudan ne suka shirya wannan dandali na kwanaki biyu.

A jawabinsa yayin taron mataimakin shugaban kasar Sudan Mista Bakri Hassan Salih ya bayyana cewa, a koda yaushe kasar Sudan tana ba da muhimmanci sosai kan aikin dakile ta'addanci, kana irin matakan da take dauka a 'yan shekaru nan sun taimaka wajen hana yaduwar ayyukan ta'addanci, musamman ma a arewacin yankin Darfur dake dab da kasar Libya.

A nasa jawabin, mataimakin babban sakataren AL Mista Ahmed Ben Helli, ya yi kira ga kasashe mambobin AL da su kara hada kai don yaki da ta'addanci. Ya ce, ya kamata kasashe mambobin kungiyar su hada kai tare da bullo da manufofin da suka dace don hana yaduwar ayyukan ta'addanci, ciki hadda matakan siyasa, aikin soja, tattalin arziki, yada labarai da dai sauransu. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China