in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta kara samun lambobin zinare biyu a gasar wasannin Olympics na Rio
2016-08-09 19:54:36 cri

A yayin da aka shiga yini na uku a gasar wasannin Olympics da ke gudana yanzu haka a birnin Rio na kasar Brazil, kasar Sin ta kara lashe lambobin zinare a wasannin linkaya da tsallen fadawa ruwa.

Sun Yang ya lashe lambar zinare a wasan linkaya na mita 200 cikin minti 1 da dakika 44.65, kuma wannan ita ce lambar zinare na farko da kasar Sin ta lashe a wannan gasa, kana lambar zinare ta uku da ya lashe a gasar ta Olylmpics.

A bangare guda kuma Lin Yue da Chen Aisen suma sun lashe lambar zinare a wasan tsallen fadawa cikin ruwa bangaren maza. Sakamakon da ke nuna cewa, kawo yanzu kasar Sin ta lashe lambobin zinare a dukkan wasannin tsallen fadawa ruwa a gasar wasannin Olympics na wannan karo.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China