in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala taro kan kokarin kare filaye da gandun daji da ke nahiyar Afirka daga bacewa a Kigali
2016-08-01 09:47:46 cri
A jiya Lahadi ne ministoci da wakilai daga kasashen Afirka suka sanya hannu kan yarjejeniyar kare filaye da gandun daji da ke nahiyar.

Taron wanda gwamnatin Rwanda tare da hadin gwiwar kungiyar kasashen gabashin Afirka da kungiyar kare muhalli ta kasa da kasa suka shirya, wata dama ce ta kare gandayen daji da ke kokarin bacewa a nahiyar Afirka sakamakon matsalar canjin yanayi.

Bayanai na nuna cewa, kasashen Afirka suna daga cikin yankunan da matsalar canjin ta fi shafa a duniya, duk da cewa nahiyar ba ta cikin yankunan da ke haddasa matsalar gurbatar yanayi a duniya.

Tun a makon da ya gabata ne mahalartar taron daga nahiyar ta Afirka suka hallara a birnin na Kigali inda suka bayyana kudurinsu na aiwatar da yarjejeniyar Bonn ta kare Eka miliyan 150 na gandun daji da filayen da aka yi watsi da su ya zuwa shekarar 2020 da kuma eka miliyan 350 ya zuwa shekarar 2030. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China