in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashe biyu na Congo sun yi kira da a yi garambawul a kwamitin sulhu na MDD
2016-06-29 19:49:10 cri
Shugaban jamhuriyar Congo Denis Sassou Nguesso da takwaransa na jamhuriyar demokiradiyar Congo(DR Congo) Joseph Kabila sun sake nanata goyon bayansu na ganin an gabatar da bukatun kasashen Afirka na ganin an yiwa kwamitin sulhu na MDD gyaran fuska.

Shugabannin sun bayyana hakan ne lokacin da suke jawabi a taron tattauna batutuwan samar da zaman lafiya da tsaro da ke damun kasashen nasu, wanda ya gudana a Oyo mai nisan kilomita 400 daga Brazzaville.

Har ila yau shugabannin sun bayyana cewa, suna goyon bayan yarjejeniyar Ezulwini, wata matsaya da aka cimma game da huldar kasa da kasa da yin gyare-gyare a MDD,wadda ta samu amincewar kungiyar tarayyar Afirka.

Ita dai wannan yarjejeniya tana kira ne da a kara wakilicin kasashen Afirka a kwamitin sulhu bisa tsarin demokuradiya, ta yadda nahiyar Afirka kamar sauran shiyoyin duniya za ta samu wakilci.

Yarjejeniyar Ezulwini tana ganin cewa, kamata ya yi nahiyar Afirka ta samu kujerun din-din-din a kwamitin sulhu na MDD da wasu kujeru guda biyu da bana din-din-din ba a kwamitin sulhun.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China