in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Cote d'Ivoire ta yi kiran da a kara hada kai a yakin da ake da ta'addanci
2016-06-28 20:04:09 cri
Firaministan kasar Cote d'Ivoire Daniel Kablan Duncan ya bukaci kasashe mambobin kungiyar ECOWAS da su kara karfafa hadin gwiwar da ke tsakaninsu ta yadda za a yaki ayyukan ta'addanci.

Duncan ya wanda ya yi wannan kiran jiya lokacin da ya ke jawabi a ofishin kungiyar ECOWAS da ke birnin Abidjan, ya bayyana cewa, muddin kasashe mambobin kungiyar suka kara yin hadin gwiwa, hakan zai taimakaa wajen magance kalubalen tsaro da shiyyar ta ke fuskanta.

Alkaluma na nuna cewa, a shekarar da ta gabata an samu karuwar hare-haren ta'addanci da ake kaiwa masu yawon shakatawa ko wuraren da baki 'yan kasashen waje suke zuwa a kasashen Afirka.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China