in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu mutanen kasar Birtaniya sun yi kira da a sake yin zaben raba gardama kan batun ficewar kasarsu daga EU
2016-06-26 13:56:33 cri

A Birtaniya mutane kimanin 300 ne suka taru a kofar majalisar dokokin kasar a jiya Asabar domin nuna rashin jin dadi kan sakamakon zaben raba gardama kan batun ficewar kasar ta Birtaniya daga kungiyar tarayyar Turai wato EU, inda suka yi kira da a sake yin zaben raba gardamar. A wannan rana kuma, babbar ministar gwamnatin Scotland Nicola Sturgeon ta nemi kungiyar EU da ta tattauna game da matsayin da yankin Scotland ke dauka a cikin kungiyar EU bayan da aka balle kasar Birtaniya daga kungiyar EU.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China