in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwararru daga Afrika zasu gana a Rwanda game da dumamar yanayi
2016-06-26 13:32:58 cri
Sama da kwararru 600 ne a fannin sauyin yanayi daga gwamnatoci na kasashen Afrika da wasu sassan kasashen duniya zasu hallara a taron dandali game da dumamar yanayi a Afrika wato ACF na wannan shekara, za'a gudanar da taron ne a birnin Kigali babban birnin Rwanda a mako mai zuwa.

Za'a gudanar da taron ne daga ranar 28 zuwa 30 ga wannan watan na Yuni, kana za'a yi nazari da kuma tattaunawa game da hanyoyin da za'a samar da cigaba mai dorewa a nahiyar.

Mahalarta taron na wannan shekara, za kuma su tabo batu game da yin hadin gwiwa tsakanin gwamnatoci da hukumomi masu zaman kansu don tara kudaden aiwatar da shirin takaita amfani da makamashi mai gurbata muhalli don samun cigaba.

Da yake zantawa da manema labarai a jiya Asabar, Vincent Biruta, minsitan albarkatun kasar Rwanda, yace kasar sa a shirye take ta karbi bakuncin taron wanda ake saran za'a tattauna yadda za'a shawo kan kalubale game da sauyin yanayi a nahiyar Afrika.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China