in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban kasar Afrika ta Kudu ya isa Lesotho
2016-06-24 11:52:18 cri
Mataimakin shugaban kasar Afrika ta Kudu Cyril Ramaphosa, a matsayinsa na mai shiga tsakani na kungiyar cigaban kasashen kudancin Afrika (SADC) ya isa tun ranar Laraba a Maseru na kasar Lesotho a karkashin wata ziyarar aiki data shafi bunkasa zaman lafiya da tsaro a wannan kasa.

Mista Ramaphosa zai yi shawarwari tare da masu ruwa da tsaki a fagen siyasa domin cigaba da kokarin tattabar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Lesotho, in ji fadar shugaban kasar Afrika ta Kudu.

Ziyarar ta mista Ramaphosa na cikin tsarin shirye shiryen zaman taron manyan jami'ai na kungiyar SADC da zai gudana a ranar 28 ga watan Yuni a Gaborone na kasar Botswana, domin tattauna matsalar Lesotho. Wannan taro zai samu halatar shugabannin Batswana, Afrika ta Kudu, Mozambique, Zimbabwe, Swaziland da Tanzaniya.

A yayin ziyarar tasa a kasar Lesotho, mista Ramaphosa zai gana da firaminista Phakalitha Mosisili da kuma mambobin gwamnatinsa, mambobin jam'iyyun adawa, kungiyar sarakunan gargajiya, kwamitin malaman cocin Lesotho da wakilan kungiyoyin fararen hula domin tattauna cigaban da aka samu wajen aiwatar da matakan da aka cimma domin kawo sauye sauye kan kundin tsarin mulki da tsaro. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China