in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala kada kuri'ar raba gardama a Birtaniya
2016-06-24 11:35:05 cri
An fara tattara akwatunan zabe a cibiyoyin tattara sakamako 380 bayan kada kuri'ar raba gardama game da kasancewar Birtaniya a EU.

Miliyoyin 'yan Birtaniya ne suka jefa kuri'unsu a rumfunan zabe kimanin 41,000 a jiya Alhamis a matsayin zaben raba gardama na yiwuwar ballewar Birtaniya ko cigaba da zama mamba a kungiyar tarayyar Turai wato EU.

An dai fara zaben ne tun da sanyin safiya da misalin karfe 7 wato karfe (0600 agogon GMT), sai dai runfunan zaben da dama basu bude da wuri ba, sakamakon ruwan sama da aka yi cikin dare a birnin Landan da ma yankunan kudu maso gabashin Ingila.

Za'a bayyana sakamakon zaben cikin dare, sai dai sakamako na karshe na zaben za'a bayyana shi ne a hukumance a babban dakin taro na Manchester Town Hall, kuma mai yiwuwa a bayyana shi da safiyar yau Juma'a agogon kasar.

Wata kididdiga da hukumar zaben kasar ta fitar ta nuna cewar mutane miliyan 46 da rabi ne suka cancanci kada kuri'u a zaben kuri'ar raba gardaman.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China