in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Congo ta yi allawadai da harin da aka kai a ofishin jakadancinta
2016-06-23 13:01:14 cri
Gwamnatin Congo ta yi allawadai a ranar Laraba kan harin da aka kaiwa ginin ofishin jakadancinta dake birnin Paris na kasar Faransa a cikin daren Litinin zuwa Talata.

A cikin wata sanarwa da aka fitar kan wannan lamari, gwamnatin Congo ta jaddada cewa harin da har yanzu ba a tantance wadanda suka aikata shi ba, ya janyo gobara a wani bangaren ginin jakadancin da kuma lalata kayayyaki da ake cigaba da kiyastawa.

Gwamnatin Congo na yin allawadai da wannan harin ta'addanci da babbar murya tare da yin kira kuma ga hukumomin Faransa da su gudanar da bincike domin tantance masu hannu kan wannan lamari tare da gurfanar dasu gaba kotu, in ji sanarwar. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China