in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Zimbabuwe ya bayyana goyon bayansa ga matsayin kasar Sin kan batun tekun kudancin kasar
2016-06-22 11:04:01 cri
Shugaban kasar Zimbabuwe Robert Mugabe a jiya Talata ya bayyana goyon bayansa ga matsayin kasar Sin a kan tekun kudancin kasar, kuma ya yi kira da a warware sabani tsakanin bangarorin da abin ya shafa ta hanyar yin shawarwari.

A yayin da shugaba Mugabe ke zantawa da mataimakin ministan harkokin waje na kasar Sin Zhang Ming a birnin Harare, ya ce, Zimbabuwe ta nuna cikakken goyon bayan ta ga matsayin da kasar Sin ke dauka a kan batun tekun kudancin kasar Sin, wato kamata ya yi kasashen da abin ya shafa su daidaita gardamar ta hanyar yin shawarwari cikin ruwan sanyi.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China