Lamarin dai ya faru ne da misalin karfe 2:20 na yammacin wannan rana a kusa da inda ake tantance fasinjoji a sashe na 2 na filin jirgin saman.
Hukumomin kula da zirga zirgar jiragen saman na Shanghai sun tabbatar da cewar wasu ababen fashewa da aka hada da hannu ne suka fashe.
Sai dai tuni aka garzaya da wadanda suka jikkatan zuwa asibiti, sannan ana cigaba da gudanar da bincike kan lamarin.(Ahmad)