in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Najeriya suna samun nasara a yakin da suke da masu tayar da kayar baya a Najeriya
2016-06-10 12:29:25 cri
Rundunar sojojin Najeriya ta bayyana cewa, dakarunta suna samun gagarumar nasara a yakin da suke yi na kakkabe 'yan ta'adda a yakin arewa maso gabashin kasar.

Kakakin rundunar sojojin Najeriya kanar Sani Usman wanda ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a birnin Lagos cibiyar kasuwancin kasar, ya ce, sojojin sun yi nasarar kashe tare da lalata maboyar 'yan ta'addan da dama. Baya ga makamai da albarusai da sauran kayan fada da sojojin suka kwatao a lokacin da suke kadamar da hare-hare kan mayakan na Boko Haram a jihar Borno kadai.

Kanar Sani ya ce, dakarun bataliya ta musamman ta 7 ta samu wannan nasara ce tare da taimakon hari ta sama daga mayakan saman kasar.,

Kakakin ya kara da cewa, sojojin sun kaddamar da hare-hare da sanyin safiyar jiya ne da nufin kawar da gyauron mayakan Boko Haram daga cikin sansanoninsu a kauyuka da dama na karamar hukumar Bama da ke jihar Borno.

Kanar Usman ya kuma bayyana cewa, an garzaya da mata da yaran da aka ceto daga hannun mayakn Boko Haram zuwa sansanonin 'yan gudun hijira daban-daban da ke jihar bayan da aka kammala tanance su.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China