in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kenya ta samu gurbin shiga gasar AFCON ta 2017
2016-06-08 09:07:54 cri
Kungiyar kwallon kafar kasar Kenya ta samu nasarar doke takwarar ta ta Congo, a kokarin da kungiyoyin kwallon Afirka ke yi na samun gurbin buga gasar nahiyar, wadda hukumar AFCON za ta shirya badi a kasar Gabon.

An dai tashi wasan da kungiyoyin biyu suka buga 2 da 1, a birnin Nairobin kasar Kenya.

A nata bangare kasar Guinea Bissau, ita ma ta doke Zambia da ci 3 da 2 a wasan da suka buga ranar Asabar. Yanzu dai Guinea Bissau ce ke kan gaba a rukunin ta, yayin da ya rage wasa daya ta kammala wasannin na share fage. Kafin wannan nasara ba a yi tsammanin Guinea Bissau za ta cimma nasarar samun gurbi a gasar dake tafe a badi ba. Sai dai nasarar da kungiyar ta samu a wasan ta na farko da Kenya, da kuma kunnen doki da Congo da Zambia suka buga har sau bi-biyu a wasannin su na baya sun sanya Guinea Bissau shigewa gaba a rukunin.

Da yake bayyana farin cikin samun wannan nasara, kocin Kenya Stanley Okumbi, wanda ya maye gurbin Bobby Williamson a watan Fabarairu, ya ce nasarar da suka samu ba tashi ba ce shi kadai, nasara ce ta 'yan wasa, da 'yan kasar Kenya baki daya. Ya ce ya tabbatar kowa na farin ciki da wannan nasara. Duk da kuma babu isasshen lokaci na gina kungiya mai karfi, amma nasarar da suka samu kan Congo ta kayatar da kowa. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China