in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana horas da jami'an kiyaye zaman lafiya na MDD
2016-06-06 19:53:37 cri
A yau ne a nan kasar Sin aka fara wani shirin horas da jami'an da ke aiki da dakarun kiyaye zaman lafiya na MDD.

Wannan shi ne karon farko da aka shirya Kwas din a kasar Sin wanda ake gudanarwa tare da hadin gwiwar sashen kula da aikin kiyayen zaman lafiya na MDD da ma'aikatar kula da harkokin tsaro ta kasar Sin.

Manyan kwararru a fannin aikin kiyaye zaman lafiya 26 daga kasashe 17 ne za su horas da kwadandoji da sojoji da ke aikin kiyaye zaman lafiya.

A yayin bikin bude kwas din, mahalartan sun tashi tsaye inda suka yi shiru domin nuna girmamawa ga sojojin da aka kashe a yayin da suke bakin aiki.

A jawabinsa yayin bikin,shugaban sashen ayyukan kiyaye zaman lafiya na MDD Herve Ladsous, ya yaba rawar da sojojin wanzar da zaman lafiya na kasar Sin suka taka a wuraren da aka tura su. Bugu da kari, ya mika sakonsa na ta'aziya ga dakarun da suka kwanta dama da wadanda suka jikkata a yayin da suke gudanar da wannan aiki.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China