in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Sin ya mika sakon taya murna ga taron ministoci karo na 7 game da makamashi masu tsabta
2016-06-03 09:26:32 cri
Daga ranar 1 zuwa ranar 2 ga wata ne, aka bude taron ministoci karo na 7 game da samar da makamashi masu tsabta da taron ministoci game da sabon aiki a birnin San Francisco da ke kasar Amurka.

A sakonsa na fatan alheri da taya murna ga taron,shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cewa, game da makomar samun bunkasuwar Sin, kasarsa za ta martaba manufar kirkiro da sabbin abubuwa, da daidaita mabambanta yankunan, da kiyaye muhalli, da bude kofa ga kasashen waje, da cin gajiyar fasahohin da aka samu, kana za ta dauki jerin matakai, don raya makamashi masu tsabta, da kyautata tsarin sana'o'i da yin amfani da makamashin ba tare da gurbata muhalli ba, da yin gine-gine da raya harkokin zirga-zirga a kasa, tare da kiyaye muhalli.

Sin za ta yi kokarin kiyaye muhalli, don sa kaimi ga zaman jituwa tsakanin Dan Adam da muhallin halittu, in ji shugaban.

Shugaba Xi ya ce, a shekara mai zuwa, Sin za ta dauki bakuncin taron ministoci karo na 8 game da samar da makamashi masu tsabta, yana fatan wakilan kasashen duniya za su zo kasar Sin, don yin mu'amala da yada fasahohin da suka samu wajen yin amfani da makamashi masu tsabta, don ci gaba da ingiza samun dauwamammen ci gaba a doron kasa.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China