in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban NPC ya gana da shugaban kasar Togo
2016-05-31 21:03:04 cri
Shugaban majalisar wakilan jama'ar kasar Sin (NPC) Mr. Zhang Dejiang, ya gana da shugaban kasar Togo Mr. Faure Essozimna Gnassingbé a yau Talata, a babban dakin taron jama'a da ke nan birnin Beijing.

A yayin ganawar tasu, Mr. Zhang Dejiang ya ce, Sin na fatan hada kai tare da Togo wajen tabbatar da daidaito game da batutuwan da shugabannin kasashen biyu suka cimma, wanda hakan zai baiwa kasar Togon damar cin gajiyar kudurorin da aka amince da su, a gun taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka da aka gudanar a birnin Johannesburg a bara.

Shi kuma a nasa bangare shugaba Faure cewa ya yi, Togo tana fatan koyi daga saurin bunkasar da Sin ta samu, tare kuma da karfafa hadin gwiwa da kasar Sin, don tabbatar da nasarorin da aka cimma a gun taron koli na Johannesburg.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China