in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude taron koli na G7 gami da zanga-zanga
2016-05-26 15:28:16 cri
A yau Alhamis 26 ga watan nan ne aka kaddamar da taron koli na kungiyar G7 a yankin Ise Shima dake kasar Japan. Yayin taron na yini biyu wasu al'ummar kasar sun gudanar da zanga-zanga bisa zargin wasu sojojin Amurka da jefar da gawar wata mace a birnin Okinawa.

Wannan shi ne karo na 2 da Japan ta sake karbar bakuncin taron kolin G7 bayan shekaru 8. Kasashe da dama za su tattauna batutuwan ciniki, da tattalin arziki na duniya, da batun 'yan gudun hijira da yaki da ta'addanci. Sauran batutuwan sun hada da na sauyin yanayi, da albarkatun ma'adinai, da zaman lafiya da karko a Asiya. Kaza lika bisa wasu manufofi da Japan ke nacewa, an yi hasashen cewa, za a tattauna batun kudancin tekun kasar Sin a yayin taron.

A gobe Juma'a za a gudanar da taron gaman gari na kungiyar ta G7, inda ake sa ran tattauna batun saka jari a fannin ababen more rayuwa. Taron da aka gayyaci shugabannin kasashen Chadi, da Indonesiya, da Sri Lanka don su halarta. Har wa yau babban magatakardar M.D.D. Ban Ki-Moon, da asusun ba da lamuni na duniya, da bankin duniya da sauran kungiyoyin duniya za su tura wakilai don halartar sa.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China