in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta soki Japan a kan yadda take rura wuta a kan batun tekun kudancin kasar Sin
2016-05-25 20:00:59 cri
Batun tekun kudancin kasar Sin ya sake jawo hankalin bangarori daban daban a yayin taron kolin kungiyar G7. A gun taron manema labarai da aka shirya a ranar 25 ga watyau Laraba a a nan birnin Beijing, kakakin ma'aikatar harkokin waje na kasar Sin Hua Chunying ta bayyana cewa, kasar Sin tana gudanar da harkoki a yankin tekun kudancinta ne bisa doka kuma yadda ya kamata, don haka, bai kamata a nuna mata yatsa ba.

An labarta cewa, ana shirin nuna kulawajanyo hankalin duniya ga harkokin da kasar Sin ke gudanarwa a tekun kudancinta a sanarwar da za a fitar a gun taron. Baya ga haka, a yayin da firaministan kasar Japan ke zantawa manema labarai tare da takwaransa na kasar Canada, ya bayyana matukar kulawarsa ga yadda kasar Sin ke gina tsibirai da gudanar da harkokin soja a yankin tekun. A game da hakan, kakakin Madan Hua ta bayyana cewa, kasar Japan ta jima da tana rura wuta a kakururuta n batun tekun kudancin kasar Sin. A yanayin da tattalin arzikin duniya da akeke ciki, kamata ya yi taron kolin G7 ya mai da hankali a kan gudanar da harkokin tattalin arziki da kuma hadin gwiwa. Amma a maimakon haka, kasar Japan a matsayinta na kasar da ke karbar bakuncin taron, tana kokarin shirya wani makirci bisa ga a taron, abin da ba zai amfana wa kungiyar G7 ba, balle ma a samu zaman lafiya a yankin tekun kudancin kasar Sin.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China