in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bankin duniya ya baiwa Kongo(kinshasa) dalar Amurka miliyan 41 don raya sha'anin kiwon lafiya
2016-05-23 11:11:19 cri
Rahotanni daga wasu kafofin yada labaru na kasar Kongo(kinshasa), sun bayyana cewa, a kwanakin baya wakilin bankin duniya da ke kasar Kongo(kinshasa) Moustapha Ndiaye, ya kulla wata yarjejeniyar hadin gwiwa da ministan harkokin kudi na kasar Henri Yav Mulang a birnin Kinshasa fadar mulkin kasar, inda bankin duniya ya amince da kudurin samar wa kasar kudin agaji, da yawansu zai kai dalar Amurka miliyan 41, don nuna goyon baya ga shirin kyautata sha'anin kiwon lafiyar kasar.

Wannan shiri zai kunshi fannoni 3, wato fannin kafa tsarin tattara bayanai don bambanta matsayin al'ummar kasar. Sai kuma kafa tsarin sarrafa magunguna. Na uku kuma shi ne batun kafa da kyautata tsarin mu'amalar nazarin bayanai.

Ministan kiwon lafiyar kasar Kongo (Kinshasa) Felix Kabange Numbi Mukwampa, ya bayyana cewa, yanzu haka kashi 1 cikin 4 na jama'ar kasar ne kadai ke da takardar haihuwa, abun da ke kawo matsalar rashin cikakkiyar kididdiga ta tsara wasu shirye-shiryen kiwon lafiya.

Gwamnatin Kongo (kinshasa) dai na fatan yin amfani da wannan shiri, wanda zai a gudanar cikin shekaru 4, don kyautata yanayin kiwon lafiya ta hanyar kididdigar bayanai game da al'ummar kasar, da samar da alkaluman da za a amince da su wajen tsara shirin raya kiwon lafiya na kasar daga shekarar nan ta 2016 zuwa shekarar 2020.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China