in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Pakistan ba ta tabbatar da rasuwar jagoran kungiyar Taliban ba
2016-05-23 10:45:31 cri
A ranar 22 ga wata, ma'aikatar harkokin wajen kasar Pakistan ta fidda wata sanarwa, wadda ke cewa sojojin Amurka sun kai hari ta sama, a yankunan kudu maso yammacin kasar dake da iyaka da kasar Afghanistan, kuma hakan ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 2, sai dai cikin sanarwar, ba a fayyace ko akwai jagoran kungiyar Taliban Akhtar Mohammad Mansour cikin wadanda harin ya rutsa da su ba.

A baya Mansour shi ne mataimakin tsohon jagoran kungiyar Taliban Mullah Mohammad Omar, kuma a ranar 31 ga watan Yulin shekarar 2015, ya zama sabon jagoran kungiyar don maye gurbin Omar, wanda ya rasu sakamakon wata rashin lafiya.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China