in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kenya za ta shirya taron UNCTAD
2016-05-20 10:25:12 cri
Za a shirya taron karo na 14 na raya cinikayya da samun bunkasuwar M.D.D. wato na UNCTAD daga ranar 17 zuwa ranar 22 ga watan Yuli a birnin Nairobi hedkwatar kasar Kenya, kuma taken taron shi ne"daukar matakai don gudanar da shirin 2030 a hukunce".

Taron UNCTAD da aka yi na wannan karo shi ne karo na farko, bayan da M.D.D. ta fidda shirin tsare-tsare da samun bunkasuwa cikin dogon lokaci na 2030 a watan Satumbar bara. Haka kuma taron zai kasance kunshe da sakamakon da aka samu a yayin taron koli karo na 10 na ministoci na kungiyar cinikayya ta duniya WTO da babban taron sauyin yanayi na Paris, da taron kolin kan tattara kudade don samun bunkasuwa na duniya, kana taron zai samar da wani dandalin yin mu'amala ga shugabanni mahalartar taron.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China