in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya gana da takwaransa na Mozambique
2016-05-18 21:26:31 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na kasar Mozambique, Filipe Nyusi, yau Laraba a babban dakin taron jama'a da ke nan birnin Beijing, inda shugabannin biyu suka yanke shawarar kara daukaka huldar da ke tsakanin kasashen biyu.

Shugaba Xi ya yi nuni da cewa, yanzu haka, kasashen Afirka na kokarin gano hanyar da ta dace su bi domin samun ci gabansu, wadanda kuma suke hada kan juna tare da gaggauta dunkulewar nahiyar, abin da ke sa kasar ta Sin farin ciki, kuma kasar na nuna imani ga makomar bunkasuwar kasashen Afirka. Ya ce kasar Sin a nata bangaren za ta yi kokarin tabbatar da nasarorin da aka cimma a gun taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka da aka gudanar a birnin Johannesburg, domin samun moriyar hadin gwiwa da juna.

A nasa tsokaci Mr. Filipe Nyusi godiya ya yi ga Sin, kan tallafin da ta ba wa kasarsa ta fuskar neman 'yancin kan al'umma, da kuma ci gaban kasar, kuma ya ce, shawarar da shugaba Xi ya gabatar game da hadin gwiwar Sin da Afirka a gun taron kolin Johannesburg, ta sanya kuzari ga ci gaban kasashen Afirka, da kuma hadin gwiwar da ke tsakanin kasashen Afirka da ma kasar Sin. Kaza lika Mozambique na fatan inganta hadin gwiwa da Sin ta fannonin ciniki da masana'antu, da aikin gona da kamun kifi, da sarrafa abinci da makamashi, da kimiyya da manyan ababen more rayuwa da sauransu. (Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China