Sanarwar ta ce, bisa bayanan sirri da bangaren 'yan sanda ya samu, an ce, wasu gungun dakarun dauke da makamai sun buya a lardin Ariana dake arewa da birnin Tunis wato hedkwatar kasar. Don haka, 'yan sandan sun kai samame wurin, inda suka yi musayar wuta da dakarun tare kuma da kwace makamai da dama.
Bisa labarin da kafofin yada labarum kasar suka bayar, an ce, a cikin wadannan dakaru, akwai wadanda ake tuhumarsu da hannu a harin da aka kai a birnin Ben Guerdane dake yankin kudu maso gabashin kasar.(Bako)