in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya taya Kim Jong-un murnar zama shugaban jam'iyyar kwadago a kasar
2016-05-10 10:59:47 cri
A ranar 9 ga wata, babban sakataren kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin Xi Jinping ya mika sako ga Kim Jong-un don taya shi murnar zama shugaban jam'iyyar kwadago ta kasar Koriya ta Arewa a yayin taron wakilan jam'iyyar karo na 7.

A madadin kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin da shi kansa, Xi Jinping ya taya murna ga Kim Jong-un game da sabon ci gaba da aka samu a kasar dake karkashin shugabancin jam'iyyar kwadago ta kasar wajen raya kasar bisa tsarin kwaminisanci na zamani.

Xi ya bayyana cewa, jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin da gwamnatin kasar suna dora muhimmanci sosai game da alakar dake tsakanin kasashen biyu. Yana kuma fatan yin kokari tare da kasar Koriya ta Arewa, domin inganta hadin gwiwar sada zumunta da ke tsakanin kasashen biyu, don kawo alheri ga kasashen biyu da jama'arsu, tare kuma da ba da gudummawa wajen samar da zaman lafiya da karko da samun bunkasuwa a shiyyar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China