in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Harin da aka kai a yankin kudancin kasar Afghanistan ya haddasa mutuwar 'yan sanda 3
2016-05-09 14:06:24 cri
A jiya lahadi ne, ma'aikatar harkokin cikin gida ta kasar Afganistan ta ce, a ranar Asabar, dakaru masu dauke da makamai sun kai hari kan wata tashar binciken ababan hawa ta 'yan sanda dake lardin Helmand a yankin kudacin kasar,harin da ya haddasa mutuwar 'yan sanda 3.

Ma'aikatar kula da harkokin cikin gida ta kasar Afghanistan ta ce, an kai hari ne a birnin Lashkar Gah hedkwatar jihar Helmand. An yi musayar wuta tsakanin 'Yan sanda da dakaru masu dauke da makamai, inda dakaru masu dauke da makamai 10 suka mutu nan take, kana 'yan sanda 4 da dakaru 10 suka ji rauni.

Lardin Helmand na kasar Afghanistan wuri ne da ake noman tabar wiwi, kuma safarar tabar wiwi ta zama hanyar da kungiyar Taliban da ke wurin ke amfani da ita don samun kudin shiga. Wannan ya sa wurin ya kasance tungar dakarun kungiyar Taliban, A watan Afrilu na bana, kungiyar Taliban ta sake kai farmaki na sabon zagaye a lokacin bazara, wannan ya sa yanayin tsaro a kasar ya sake tabarbarewa.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China