in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Amurka da Rasha sun daddale yarjejeniyar tsagaita bude wuta a yankin Allepo na Siriya
2016-05-05 10:29:35 cri
A jiya Laraba ne, majalisar gudanarwar Amurka ta ba da wata sanarwa cewa, kasashen Amurka da Rasha sun daddale yarjejeniyar tsagaita bude wuta tsakanin bangarorin da batun Siriya ya shafa a birnin Allepo da sauran unguwannin dake kusa da wurin, ta yadda za a sassauta halin kunci da wadannan wurare suka fuskanta a kwanan baya.

A cikin sanarwar, kakakin majalisar gudanarwar Amurka Mark Toner ya bayyana cewa, Amurka tana fatan Rasha a matsayinta na shugabar rukunin kula da batun tsagaita bude wuta game da batun Siriya na kasa da kasa za ta ci gaba da matsa lamba ga gwamnatin Siriya ta martaba yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma, yayin da Amurka za ta bukaci bangaren 'yan adawa na kasar da su ma su yi hakan.

A jiya ne, sojojin Siriya suka sanar da cewa, tun daga karfe 1 na safiyar yau Alhamis, za su tsagaita bude wuta har na tsawon sa'oi 48 a yankin Allepo da ke yankin arewacin kasar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China