in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hare-haren da aka kai a yankin gabashin kasar Kongo(Kinshasa) sun haddasa mutuwar mutane 17
2016-05-05 09:58:38 cri
Kakakin sojojin gwamnatin Kongo(kinshasa) Mac Azukayi ya bayyana cewa, wasu dakaru dauke da makamai sun kai hare-hare kan kauyuka guda 2 da ke lardin Arewacin Kivu a yankin gabashin kasar Kongo(kinshasa) a ranar Talata da dare, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane a kalla 17.

Mazauna wurin suna ganin cewa, dakarun ADF dake adawa da gwamnatin Uganda ne suka kai wadannan hare-hare.

Yankin gabashin kasar Kongo(kinshasa) dai yana makwabtaka da kasar Uganda. Dakarun ADF sun dade suna zaune a cikin kasar Kongo(kinshasa), kuma su kan kai hare-hare kan sojojin gwamnatin da jama'a.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China