in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hare-haren da aka kai a yankin Halep ya haddasa mutuwar mutane da wadanda suka jikkata sama da 10
2016-05-04 10:58:59 cri
A ranar 3 ga wata, sojojin Siriya sun ba da sanarwa cewa, kungiyoyin masu dauke da makamai sun kai farmaki a yankin Halep da ke arewacin Siriya, inda suka jefa igwa a unguwanni masu cinkoson jama'a, lamarin da ya haddasa mutuwar mutane da wadanda suka jikkata sama da 10.

Kamfanin dillancin labarun Siriya ya ruwaito cikin sanarwar da sojojin Siriya suka fitar cewa, a wannan rana, kungiyoyin masu tsattsauran ra'ayi sun kai farmaki ga sojojin Siriya. An jefa igwa a unguwannin jama'a da wani asibitin dake birnin Halep. Bisa kwarya-kwaryar kididdigar da aka samu, an ce, harin igwar ya haddasa mutuwar mutane a kalla 20, tare da jikkatar wasu 40, akasarinsu mata ne da yara.

A wannan rana, bayan da ministan harkokin wajen Rasha Sergei Lavrov ya yi shawarwari da manzon musamman na sakatare janar na M.D.D. game da batun Siriya Staffan de Mistura, ya fadawa manema labaru cewa, ba za a kawar da yiwuwar shirya taron kasa da kasa kan nuna goyon baya ga kasar Siriya ba, don tattauna matakan da za a dauka wajen ingiza farfado da shawarwari. Lavrov ya ce, ya zama dole a gudanar da kudurorin da aka cimma a yayin taron, ciki har da ka'idar da ake bi domin alummar Siriyar su warware rikicin da ya addabi kasarsu. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China