Shugaba Buhari ya bayar da wannan umurni ne jiya Laraba a Abuja, babban birnin kasar yayin bikin kaddamar da wani littafi, inda ya umarci jami'an tsaron biyu da su kawo karshen dukkan kungiyoyin da ke yiwa jama'a barazana a kasar.
Ya kuma bayyana kudurin gwamnatinsa na magance wannan matsala, yana mai cewa, gwamnatinsa ba za ta lamunci irin wadannan hare-hare su ci gaba da faruwa ba.
Don haka ya kabulanci daukacin 'yan Najeriya, da su kasance masu kaunar kasarsu, ta hanyar rashin nuna bambancin kabila,addini da kuma ra'ayin siyasa, sannan su jingine duk wani ra'ayi kan marudun kasa.
A ranar 5 ga watan Maris ne wasu da ake zaton Fulani makiyaye ne suka kona wasu al'ummomi 7 kurmus a yankin Agatu dake arewa maso tsakiyar jihar Benue tare da kashe wasu daruruwa.
Sai dai wasu makiyayan da suka zanta da manema labarai, sun bayyana cewa, rikicin ya barke ne bayan da wasu 'yan kabilar ta Agatu suka kashe musu dabbobinsu kimanin 10,000.(Ibrahim)