Jami'in ya bayyana hakan ne yayin taron kasashen Sin da Afirka da ya gudana jiya Laraba a birnin Abuja, fadar mulkin Najeriya.
Ya ce kokarin da gwamnati mai ci a Najerya ke yi na farfado da yarjeniyoyin da ke tsakanin sassan biyu da kara kulla wasu sabbi, ya sanya manufofin kasashen waje na kasar aza kasar Sin a muhimmin matsayi.
Ya kara da cewa, karfafa hadin gwiwa tsakanin Najeriya da Sin, za ta inganta harkokin masana'antu a Najeriya, matakin da a cewarsa zai baiwa masu sha'awar zuba jari a bangaren masana'antu damar cimma bukantunsu sakamakon bunkasuwar hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu. (Ibrahim)