in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi karamin taron manema labaru game da shwarwari tsakanin jam'iyyun kasar Sin da kasashen Larabawa
2016-04-21 11:28:47 cri
A ranar 20 ga wata, a birnin Yinchuan, an yi karamin taron manema labaru game da yin shawarwari tsakanin jam'iyyun kasar Sin da kasashen Larabawa. A yayin taron, mataimakin direkta na sashen kula da tuntubawar kasashen waje na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin Zhang Weijian ya bayyana hujjar shirya wannan taro, da yanayin da ake ciki game da hadin gwiwa tsakanin jam'iyyun kasar Sin da kasashen Larabawa.Mataimakin direktan kula da batun harkokin waje na jihar Ningxia mai cin gashin kanta ya bayyana ci gaba da jihar ta samu, da hadin gwiwa da kasashen Larabawa a fannoni da dama.

Zhang Jianwei ya ce, kasar Sin da kasashen Larabawa na da dankon zumunci a tsakaninsu, kuma jam'iyyun Sin da kasashen Larabawa sun kara inganta mu'amala a tsakaninsu. A farkon wannan shekara, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ziyarci yankin Gabas ta tsakiya, inda ya yi muhimmin jawabi a cibiyar kawacen kasashen Larabawa, ya nuna cewa, kasar Sin tana maraba da shugabannin kasashen Larabawa don su kai ziyara a kasar Sin, wannan taron da za a shirya ya zama matakin da aka dauka don gudanar da sakamakon da ziyarar shugaban Xi ya cimma.

A ranar 21 ga wata, za a kaddamar da taron a birnin Yinchuan, wakilai za su tattauna batutuwan "Zabin hanyar samun bunkasuwa", da tabbatar da zaaman lafiya da karko, da dangantakar dake tsakanin Ziri Daya da Hanya Daya, da jami'yyun gida da waje.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China