Babban sakatare a ma'aikatar lafiyar kasar Nicholas Muraguri yace, kimanin 'yan kasar dubu 13 da 299 ne suka kamu da cutar a fadin kasar.
Sai dai yace gwamnatin kasar, ta dauki kwararan matakan dakile ci gaba da yaduwar cutar, tun bayan samun rahoton bullar cutar na farko a birnin Nairobi.
A cikin makon jiya, an samu sabbin bayanai na wadanda suka kamu da cutar kimanin 259, a wasu daga cikin cibiyoyin kiwon lafiya na kasar.
Mahukuntan kasar sun bullo da wasu sabbin dabaru na binciko wadanda suka kamu da cutar a baya bayan nan, don daukar matakan dakile cutar cikin gagggawa, sannan an samar da kayayyakin tsabtace ruwan sha da kuma killace rijioji a matsayin wani bangaere na kandagarkin yaduwar cutar.