in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Sin ya mika sakon taya murna ga taron makamashin nukiliya a yankin tekun Fasific karo na 20
2016-04-06 13:48:04 cri
A yau Laraba ne firaministan Sin Li Keqiang, ya mika sakon taya murna ga mahalarta babban taro karo na 20, game da makamashin nukiliya na yankin tekun Fasific dake gudana a nan birnin Beijing.

A cikin sakon, firaministan Li ya ce, raya kimiyya da fasaha a fannin nukiliya ya zama muhimmin ci gaba da dan Adam ya samu a karni na 20. Ya ce amfani da makamashin nukiliya ta hanyar lumana ya taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da samun isassun makamashi, da sa kaimi ga raya tattalin arziki, da warware batun sauyin yanayi, da kawo alheri ga jama'a da dai sauransu.

Li Keqiang ya kara da cewa, gwamnatin Sin ta dora muhimmanci sosai kan raya makamashin nukiliya, da nace kan amfani da nukiliya don samar da wutar lantarki yadda ya kamata. Kana ta kafa tsarin raya masana'antu ta fasahar makamashi, za kuma ta yi hadin gwiwa da kasashen duniya wajen amfani da makamashin nukiliya ta hanyar lumana, a karkashin inuwar zaman tare, da hadin gwiwa don samun nasara tare. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China