in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumomin Sin da Nijeriya sun hada hannu don warware matsalar abinci a Afrika
2016-04-06 11:15:19 cri
Bisa rahoton da kafofin yada labaru na kasashen Afrika suka bayar, an ce, cibiyar nazarin aikin gona a wurare masu zafi ta kasa da kasa ta Nijeriya wato IITA da kwalejin nazarin aikin gona a wurare masu zafi na kasar Sin CATAS sun kafa dangantakar hadin gwiwa a tsakaninsu, don kyautata matsalar samar da isasshen abinci a nahiyar Afrika, gami da samar da guraben aikin yi ga matasa.

Shugabar cibiyar IITA Katherine Lopez ta ce, bangarorin biyu sun amince da inganta hadin gwiwa wajen kyautata amfanin gona, kamar su doya, da ayaba, da kayan lambu da coco da dai sauransu. Ta kara da cewa, za a iya taimakawa kasashen Afrika wajen habaka aikin gona ta hanyar amfani da shirin mu'amalar dalibai da masu nazari na Sin da Afrika a karkashin inuwar hadin gwiwa.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, nan gaba, hukumomi biyu, za su kara hadin gwiwa da kamfanin aikin gona ba tare da gurbata muhalli ba na kasashen yammacin Afrika wato GAWAL, don yalwata hadin gwiwa dake tsakanin cibiyar IITA da sauran hukumomin nazarin aikin gona na kasar Sin.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China