in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rashawa na mayar da nahiyar Afirka baya, in ji ministan kudin kasar Namibia
2016-04-04 13:08:59 cri
Ministan kudin kasar Namibia Calle Schlettwein, ya bayyana cin hanci da rashawa, a matsayin manyan dalilan da ke haifarwa kasashen nahiyar Afirka da koma baya.

Mr Schlettwein ya bayyana hakan ne a jiya Lahadi, yayin kaddamar da taron fidda rahoto, game da harkokin jagoranci a nahiyar Afirka karo na 4 a birnin Addis Ababan kasar Habasha.

Ministan ya kara da cewa cin hanci da rashawa ya kai matakin koli a nahiyar Afirka, musamman ma a kasahen dake fama da yake-yake, da masu tarin arzikin ma'adanai.

Rahoton da aka gabatar dai na kunshe da awon mizanin ayyukan cin hanci da rashawa, yana kuma haskaka matsayin wannan matsala, da tasirin ta ga huldar kasa da kasa.

An kaddamar da rahoton ne dai yayin bikin makon ci gaban nahiyar Afirka, wanda kungiyar ECOWAS da AU suka shirya, zai kuma gudana tsakanin ranekun 31 ga watan Maris zuwa 5 ga watan nan na Afirilu.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China