in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WHO ta bada umurnin gudanar da wani kamfen allura a Guinee bisa fargabar sake barkewar Ebola
2016-04-03 12:34:12 cri
Kungiyar kiwon lafiya ta duniya (WHO) ta umurci wani kamfen allura a kasar Guinee inda aka gano wasu mutane takwas dake dauke da cutar Ebola wadanda daga cikinsu bakwai suka mutu tun cikin karshen watan Febrairu lamarin da ya janyo fargaba game da yiwuwar sake barkewar wannan cuta a kasar, a cewar wata sanarwar cibiyar kungiyar da aka fitar a ranar Jumm'a. Sanarwar ta ce, daruruwan mutane da ake fargabar sun yi mu'amala tare da wadannan marasa lafiya takwas da suka kamu da cutar Ebola a yankunan Nzerekore da Macenta, dake kudancin Guinee, sun samu wata allurar gwaji domin dakile barkewar cutar ta baya bayan nan a cikin kasar. (Maman Ada)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China