in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD ya yi kira da a ci gaba da shimfida zaman lafiya a yankin gabar teku
2016-04-01 11:18:35 cri

Kwamitin sulhu na MDD ya bayar da sanarwa a jiya Alhamis, inda aka nuna bakin ciki kan aikin gudanar da takardar tsarin hadin gwiwa na kiyaye zaman lafiya da tsaro a kasar Congo Kinshasa da yankunan gabar teku da aka kulla tun a shekarar 2013, an kuma ba da shawarwari kan batutuwan da suka shafi kiyaye zaman lafiya da yunkurin siyasa da hako makamashi ba bisa doka ba da kuma yanayin jin kai a yankin gabat teku.

Bugu da kari, sanarwar ta ce, kwamitin sulhu na MDD ya jaddada cewa, dole ne a tarwatsa dukkan kungiyoyin tada kayar baya a gabashin kasar Congo Kinshasa, da ingiza kasashen Congo Kinshasa da Uganda da kuma Ruwanda su mika tsoffin dakarun da suka aikata laifin M23 koma kasashensu, da hana tilasta kananan yara shiga aikin soji, da sa kaimi ga kasashe daban daban da su shiga yunkurin shimfida zaman lafiya ta hanyar siyasa, da kuma katse hanyar ciniki ta dakaru wajen samu riba ta hanyar hako makamashi ba bisa doka ba.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China