A ranar jumma'an nan 25 ga wata, an yi taron kyautata ingancin ayyukan masa'anatun gwamnati na kasar Sin a nan birnin Beijing, inda firaministan kasar Li Keqiang ya bayyana cewa, a wannan shekara, Sin za ta fuskanci kalubale mai tsanani wajen samun bunkasuwa, don haka ya kamata masana'antun gwamnatin kasar su taka rawar a zo a gani wajen raya tattalin arziki da zamantakewar al'umma, don sauke nauyin da ke gaban su, da daukan hakikanin matakai, don shiga sahun gaba wajen kyautata ingancin ayyukansu.(Bako)