in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi ya jagoranci taron hukumar siyasa ta kwamintin tsakiya na kasar Sin
2016-03-26 12:56:19 cri
A ranar Jumma'an nan, hukumar siyasa ta kwamintin tsakiya ta jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin ta shirya wani taro, inda aka zartas da shiri game da yadda za a raya tattalin arziki da tsaron kasa baki daya da kuma shirin raya tattalin arziki a yankin tekun Yangtse na kasar Sin.

A yayin taron wanda babban sakatare na kwamintin Xi Jinping ya jagoranta an bayyana cewa, bunkasa harkokin sojoji da na jama'a ya zama wani babban sha'anin aikin kasar Sin, shi ne kuma babban shiri da kwamintin tsakiya ta jam'iyyar kwaminis ta tsara daga dukkan fannoni, kamata ya yi a inganta samun daidaituwar bunkasuwar tattalin arziki da harkokin tsaron kasa yadda ya kamata.

A gun taron, an nuna cewa tekun Yangtse uwar tekun al'ummar Sin, shi kuma ya zama wani jigon raya tattalin arzikin Sin. Don haka a lokacin da ake tsara shirin raya yanki, ya kamata a yi la'akari da kiyaye muhalli, domin bai kamata a raya shi fiye da kima ba.

Ya kamata a raya yankin bisa sharadin kiyaye muhalli, da inganta aikin raya yankin daga duk fannoni kuma cikin dogon lokaci, da kyautata ingancin raya aikin. Kamata ya yi a yi amfani da hanyoyin ruwa na kogin, don raya sana'o'i da kasuwanni.

A wajen taron har ila yau an lura ya kamata a tsara shiri daga manyan fannoni, don raya yankin dake kogin Yangtse da zai zama wani zirin tattalin arziki mai kyakkyawan muhalli, da daidaituwar bunkasuwar tattalin arziki.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China