in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala zagayen baya bayan nan na tattaunawa game da rikicin Syria
2016-03-25 09:36:47 cri
Sassan da rikicin kasar Syria ya shafa sun kammala zagayen tattaunawarsu na wannan karo a jiya alhamis, tare da gabatar da wasu batutuwa 12 ga sassan gwamnati da na 'yan adawa domin sake nazarta su.

Da yake gabatar da batutuwan ga sassan biyu, jakadan MDD a Syria Staffan de Mistura, ya ce tattaunawar da aka yi ta baiwa masu ruwa da tsaki damar musayar yawu, game da wasu lamurra wadanda sassan kasar suka amince da su game da makomar kasar su a nan gaba.

Wata sanarwa da tsagin 'yan adawar kasar ta Syria suka fitar, ta rawaito Mr. De Mistura na bukatar ma'aikatan ofishin sa, da su tattara bayanai na sassan da wadannan bangarori biyu suka amincewa, domin samun damar tsara zagayen taro na gaba, wanda zai maida hankali ga sauyin jagorancin kasar a siyasance.

Takardar da aka gabatarwa sassan biyu dai na kunshe da tsokaci game da amincewar su, da bukatar aiwatar da daukacin kudurorin kwamitin tsaron MDD na 2254, da na sanarwar ISSG ta taron birnin Geneva, matakin da a cewar su shi ne zai zamo jigo na warware takaddamar siyasar kasar.

Daukacin sassan biyu sun kuma jaddada daukar matakan siyasa, a matsayin hanya daya tilo ta wanzar da zaman lafiya a kasar, kana da batutuwa 12 da aka gabatar, a matsayin ginshikin kafuwar kasar Syria mai kunshe da muradun al'ummar ta.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China