in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba da firaministan Sin sun mika sakon ta'aziyya ga kasar Belgium kan harin ta'addanci a Brussels
2016-03-23 18:59:54 cri
A jiya Talata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya mika sakon ta'aziyya ga Sarkin kasar Belgium Phillipe kan abkuwar jerin hare-haren ta'addanci a birnin Brussels, inda ya yi Allah wadai kan wadannan danyun ayyuka, da nuna ta'aziyya ga wadanda suka mutu, tare da jinjinawa iyalansu da wadanda suka jikkata.

A cikin sakonsa, shugaba Xi ya furta cewa, ta'addanci abokin gaba ne ga dan Adam , wanda zai yi barazana ga kasa da kasa baki daya. Sin na fatan karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu a fannonin tsaro da yaki da ta'addanci, domin sa kaimi ga daidaita wannan batu yadda ya kamata, da nuna kiyayya ga ko wane irin ta'addanci, da zummar tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasashen biyu, har ma a duniya baki daya.

A nasa bangare, firaminista Li Keqiang ya mika sakon ta'aziyya ga takwaran aikinsa na Belgium kan wannan batu.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China