in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Sin zai halarci taron tattaunawar shekara-shekara na Asiya wato Bo'ao na 2016
2016-03-17 13:40:39 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin Lu Kang, ya furta cewa, firaministan Sin Li Keqiang, zai halarci taron tattaunawar shekara-shekara na Asiya wato Bo'ao na bana wanda za a yi a ranar 24 ga wata, inda kuma zai gabatar da jawabi.

Shugabannin kasashe Vietnam, Laos, Cambodiyan, Thailand, da Myanmar wato kasashe 5 da kogin Mekong ya ratsa su, wadanda za su halarci taron na hadin gwiwa tsakanin kogin Mekong da na Langcang.

Kaza lika firaministan kasar Nepal Khadga Prashad Oli, da takwaransa na kasar Lithuania Algirdas Butkewiczius, da na kasar Belgium Charles Michel, da mataimakin shugaban kasar Indonesiya Jusuf Kalla, da mataimakin firaministan kasar Koriya ta Kudu kuma ministan kula da tsare-tsare da kasafin kudi na kasar Yoo II-ho, da mataimakin firaministan kasar Rasha Arkaji Dvorkovich, suma ake sa ran za su halarci taron.

A wata sabuwa kuma, bisa goron gayyatar da firaministan Sin Li Keqiang ya yi, takwaransa na kasar Nepal Oli da na kasar Belgium Michel, za su kawo ziyarar aiki nan kasar Sin a hukunce baya ga halartar taron. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China