in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi: Akwai bukatar gudanar da gyare-gyare domin bunkasa yankin masana'antun arewa maso gabashin kasar Sin
2016-03-07 20:45:47 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana bukatar zurfafa gyare-gyare, domin cimma burin kawo sauyi mai ma'ana ga yankin masana'antun kasar Sin wadanda ke arewa maso gabashin kasar.

Shugaban wanda ya zanta da wakilan al'ummar lardin Heilongjiang yayin taron majalisar wakilan jama'ar duk kasa dake wakana yanzu haka a nan birnin Beijing, ya bukaci wakilan da su maida hankali ga lalubo hanyoyin samar da ci gaba, ta hanyar kirkire-kirkire bisa tsari, irin wadanda ba sa cutar da muhalli, wadanda kuma za su haifar da ci gaba na bai daya.

Mr. Xi jinping ya kara da cewa ya zama wajibi wakilan kananan hukumomi, da wakilan jam'iyya, su yi riko da dokokin kasa a yayin da suke aiwatar da sauye-sauye, a kuma gabar da suke nusar da sauran al'umma da aiwatar da hakan.

Ya ce ya dace a ci gaba da daga matsayin jami'an da suka nuna kwazo, gaskiya da rikon amana, a matsayin hanyar karfafa gwiwar su.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China