in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara aikin musayar 'yan jaridu a tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika na shekarar 2016
2016-03-07 10:44:23 cri

Jaridar Cameroon Tribune ta ba da labari cewa, an fara shirin musayar 'yan jaridu a tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika na shekarar 2016 a nan birnin Beijing, manema labaru fiye da 19 da suka fito daga kasashen Afrika dabam dabam, sun fara samu horo da yadda ake nemo labarai a cikin watanni 10 masu zuwa a kasar Sin. An gudanar da wannan aiki ne domin kara wa manema labaru na kasashen Afrika sani kan bunkasuwar hulda a tsakanin Sin da kasashen Afrika da kuma yada labarai game da hadin gwiwar bangarorin biyu. Ban da haka kuma, wadannan manema labaru na kasashen Afrika za su kara sani kan manufofin harkokin waje da kuma bunkasuwar da kasar Sin ta samu a dukkan fannoni, kana za su kai ziyara a wurare daban daban na kasar Sin.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China