in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Aljeriya ta tsare wani mutum da aka tuhuma da alaka da hare-haren birnin Paris
2016-02-29 10:10:21 cri
A 'yan kwanakin baya ne wata kotun dake birnin Bejaia na kasar Aljeriya, ta fidda wata sanarwar, dake cewa ana tsare da wani mutum da ake zargin dan ta'adda ne. Mutumin mai rike da fasfon kasar ta Aljeriya da kuma Belgium, ana zargin yana da alaka da daya daga wadanda suka kai hare-haren ta'addanci a birnin Paris dake kasar Faransa a watan Nuwambar bara.

Sanarwar ta kara da cewa, wannan mutum mai suna Zahir Mehdaoui, dan shekara 29 ya zauna a birnin Brussels dake kasar Belgium, a yanzu kuma ana tsare da shi ne a gidan kaso, bisa zargin da ake masa na da alaka da ta'addanci. An ce Mehdaoui da daya daga maharan na birnin Paris Abdel hamid Abaaoud suna da alaka ta kusa.

A daren ranar 13 ga watan Nuwambar shekarar 2015 ne aka kaddamar da hare-haren ta'addanci a birnin Paris dake kasar Faransa, lamarin da ya haddasa mutuwar mutane a kalla 130, tare da jikkatar wasu sama da 350. A kuma ranar 18 ga watan Nuwamba, a cikin matakin da bangaren 'yan sandan Faransa ya dauka, aka harbe Abdel har lahira, mutumin da ake zargi da kaddamar da harin ta'addancin na birnin Faris.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China