in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Sin ta gabatar da takarda ta farko game da matakan daikile hadarin nukiliya
2016-02-22 09:59:44 cri

A ranar Laraba 29 ga watan Janairun shekarar 2016 ne, mahukunan kasar Sin suka fitar da wata takardar bayani game da sabbin matakan dakile hadarin dake shafar nukiliya. Masanan a wannan fannin suna ganin cewa, karfin dakile hadarin nukiliya na kasar Sin zai kara inganta idan har aka kara kyautata dokoki da manufofin da abin ya shafa tare kuma da kara karfafa matakan tabbatar da tsaron aikin samar da wutar lantarki ta hanyar yin amfani da makamashin nukiliya.

Alkaluma na nuna cewa, wutan lantarkin da ake samarwa ta hanyar yin amfani da makamashin nukiliya makamashi shi ne mafi tsabta da kuma inganci. A halin da ake ciki yanzu, injunan samar da wutar lantarki ta hanyar amfani da makamashin nukiliya a babban yankin kasar Sin sun kai 30, a inda suke samar da wutar lantarki da yawansa ya kai kilowatts miliyan 28.31, ban da haka, injunan da ake kafawa a halin yanzu sun kai 24, yawansu ya kasance a sahun gaba a duniya.

Masana sun bayyana cewa, abu mafi muhimmanci yayin da ake kokarin raya fasahar samar da wutar lantarki ta hanyar amfani da makamashin nukiliya shi ne tabbatar da tsaron aikin a ko da yaushe.

Takardar da gwamnatin kasar Sin ta fitar game da yadda za a dakile aukuwar hadarin dake shafar nukiliya, ita ce takarda ta farko da kasar ta Sin ta fitar a tarihi, kuma ta kunshi fannoni takwas, inda musamman ta yi bayyani kan yadda kasar Sin ta dauki matakai domin dakile hadarin da kuma sakamakon da kasar ta samu a wannan fannin.

A kokarin ganin haka ta cimma ruwa a wannan fannin, yanzu haka an kafa tawagogin kwararru guda 25 dake kunshe da ma'aikata daga sassan sana'o'i daban-daban sama da 1300, ban da haka kuma za a kafa wata tawaga ta musamman mai wakilai 320 domin samar da agajin gaggawa a duk lokacin da aka samu hadurran da ke da nasaba da nukiliya. (Ibrahim, Mamane Ada, Saminu Alhassan, Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China